Bakonmu A Yau

IPMAN ta yaba wa Dangote na fara rarraba man fetur da Disal zuwa sassan ƙasar

Informações:

Sinopsis

Ƙungiyar dillalan man fatir masu zaman kansu ta Najeriya IPMAN ta yaba da sabon shirin matan man Dangote na fara rarraba man fetur da Disal daga Lagos zuwa sassan ƙasar, sai dai ta ci gaba da nuna damuwa kan sabon harajin naira 12,500 da gwamnatin jihar Lagos ta sanya kan duk mota guda kafin bin titin Lekki da ke kaiwa matatar Dangote da sauran kamfanonin mai dake yankin, matakin da ya haifar da fargabar samun karin faranshin litar mai, masamman a arewacin ƙasar. Sai dai a tataunawarsa da Ahmad Abba, shugaban ƙungiyar IPMAN, Alhaji Abubakar Maigandi, ya ce bayan ɗan yajin aikin da derebobin dakon mai suka yi, gwamnatin Lagos ta sanya ranar Yau Alhamis, domin cimma matsaya kan wannan batu. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawarsu................