Bakonmu A Yau
Farfesa Bello Bada akan kisan ƴanbindiga 100 da sojin Najeriya suka yi
- Autor: Vários
- Narrador: Vários
- Editor: Podcast
- Duración: 0:03:29
- Mas informaciones
Informações:
Sinopsis
Sojojin Najeriya sun yi nasarar hallaka ƴanbindiga sama da 100 a ƙaramar hukumar Bukkuyum dake jihar Zamfara, sakamakon wasu hare haren sama da suka kaddamar a kan su. Rahotanni sun ce sojojin sun yi amfani da bayanan asiri ne wajen kai harin kan ƴanta'addan waɗanda aka ce yawansu ya kai 400 a dajin a Makakkari. Wannan na daga cikin nasarorin da sojojin Najeriya suka samu a ƴan kwanakin nan. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ad Farfesa Bello Bada na Jami'ar Usman Danfodio dake Sokoto, wanda ya ce wannan shi ne labarin da ƴan Najeriya ke farin cikin ji. Ga yadda tatatunawar su ta gudana a kai.