Bakonmu A Yau

  • Autor: Vários
  • Narrador: Vários
  • Editor: Podcast
  • Duración: 1:15:04
  • Mas informaciones

Informações:

Sinopsis

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.

Episodios

  • Kan dalilan da ke sanya ƴan Najeriya faɗawa hannun ƴan damfara ta hanyar kuɗaɗen internet

    17/04/2025 Duración: 03min

    Dubban ‘yan Najeriya ne a cikin makon nan suka shiga cikin tashin hankali, sakamakon hasarar sama da Naira Tiriliyan 1 da suka tafka, a dalilin rushewar shafin CBEX, wanda ke hada-hadar kuɗaɗen Intanet. Shafin, ya ja hankalin mutane ne ta hanyar yi musu alƙawarin kason ribar 100 bisa 100 akan dukkanin adadin kuɗin da suka sanya cikinsa da zarar an cika kwanaki 30.  Sai dai bayan ɗaukar wani ɗan lokaci, shafin tare da wakilansa da ke Najeriya suka yi layar zana.Kan wannan lamari, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Sagir Muhd mataimakin shugaban ƙungiyar ƙwararru kan na’ura mai ƙwaƙwalwa ta Najeriya......Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar

  • Tattaunawa da masani Umar Saleh Anka kan ambaliyar ruwa a jihohin Najeriya 30

    15/04/2025 Duración: 03min

    Gwamnatin Najeriya ta yi gargaɗin cewa jihohi 30 na ƙasar na fuskantar barazanar iftila’in ambaliyar ruwa yayin da daminar bana ta soma, kuma tuni ta fara shirin ƙaddamar da gangamin wayar da kan mutane game da illar ta da kuma hanyoyin rage kaifinta. To ko wace rawa hukumomi da al’umma za su taka dangane da rage mummanar illar da ambaliyar ke yi?Hauwa Halliru Gwangwazo ta tattauna da Umar Saleh Anka na ƙungiyar rajin kare muhalli a Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar

  • Tattaunawa da Janjouna Ali Mahaman Sani kan zaɓen Gabon na gobe Asabar

    11/04/2025 Duración: 03min

    A kasar Gabon, ana ci gaba da yakin neman zabe a yau da ke jajiberin zaɓen Shugaban ƙasar,wanda ya haɗa 'yan takara takwas. Gwamnati ta ayyana ranar zaben gobe a matsayin ranar hutu, domin baiwa masu rajista a larduna damar yin balaguro.Ƴan adawa sun bayyana damuwarsu ganin ta yada shugaban majalisar sojin kasar ke amfani da kadarorin gwamanti a yakin zaben.Abdoulaye Issa ya tattauna da Janjouna Ali Mahaman Sani, masani siyasar kasar ta Gabon da kewaye.Ga kuma yada zantawar tasu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

  • Abdoul Moumouni Abass kan rikicin Aljeriya da ƙasashen Ƙungiyar AES

    10/04/2025 Duración: 03min

    Rikici tsakanin Mali da Aljeriya na cigaba da ɗaukar saban salo, tun bayan da Aljeriya ta kakkaɓo wani jirgin sojin Mali mara matuƙi a kan iyakar ƙasashen biyu a farko makon jiya. Sai dai wani batu da ya baiwa kowa  mamaki shi ne, yadda Nijar ta shigo cikin rikicin a matsayinta na mamba a ƙungiyar  AES, wato saban kawance da ƙasashen  Mali, Burkina Faso da Nijar suka kafa bayan ficewrasu daga ECOWAS.Umar Sani ya tattauna da Abdoul Moumouni Abass mai sharhi kan siyasar ƙasa da ƙasa.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

  • Tasirin harajin da Trump ya ɗorawa ƙasashen duniya a kan Afirka

    08/04/2025 Duración: 03min

    A Laraba 9 ga watan Afrilu, sabon harajin da ya kama daga kashi 10 zuwa sama, da shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙaba wa ƙasashen Afirka zai fara aiki, bayan da harajin da ya shafi sauran ƙasashe ya soma aiki a ranar 5 ga watan na Afrilu.  Tun cikin makon jiya ne dai matakin na Trump ya soma tasiri a kasuwannin Turai da Asiya, a yayin da ƙasashen Afirka suka shiga zulumi dangane da makomarsu.Don jin tasirin da sabon harajin na Amurka zai yi a kan tattalin Arzikin arziƙin ƙasashen Afirka, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dr Ƙasim Garba Kurfi.A latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar zanatawar.

  • Dakta AbdulHakim Garba Funtua akan harajin da Trump ya lafta wa duniya

    03/04/2025 Duración: 03min

    Ƙasashe da dama ciki har da na Ƙungiyar EU, sun alwashin mayar da martanin ƙaƙaba wa kayayyakin Amurka haraji, kamar yadda shugaba Trump ya ƙaddamar da sabon tsarin karɓar harajin da ya ce ya shafi duniya baki ɗaya.Sabon harajin dai ya kama ne daga kashi 10 zuwa sama, wanda ya shafi hajoji daga kowace ƙasa, matakin da Trump matakin ya ce ya ɗauka ne don kare buƙatun al’ummar Amurka. Don jin yadda masana ke kallon sabon yaƙin kasuwancin, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta AbdulHakim Garba Funtua.

  • Injiniya Safiya Sanusi: Kan sallamar Mele Kyari daga shugabancin NNPC a Najeriya

    02/04/2025 Duración: 03min

    Kamar yadda wataƙila aka ji cikin labarun duniyar da suka gabata, shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi tankaɗe da rairaya a fannin man fetur ɗin ƙasar inda ya sallami shugaban kamfanin NNPCL malam Mele Kyari da shugaba da mambobin majalisar aminattu na kamfanin. Nan take ne kuma shugaba Tinubun ya maye gurbin manyan jami’an da ya sallama. Ko yaya ƙwararru ke kallon wannan sauyi? Wakilinmu a Abuja Muhd Sani Abubakar ya tattauna da Injiniya Safiyya Sanusi, ƙwararriya a fannin man fetur da Iskar Gas.Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirar

  • Alhaji Abubakar Maigandi kan tasirin daina sayarwa Ɗangote man fetur da Naira

    02/04/2025 Duración: 03min

    Gidajen man fetur a Najeriya na ci gaba da sauya farashi, bayan da matatar Dangote ta sanar da cewa yarjejeniyar da ke tsakaninta da NNPC wadda ke bayar da damar samun gurbataccen mai a farashin Naira ta kawo ƙarshe ba tare da an sabunta ta ba. Alhaji Abubakar Maigandi, shugaban ƙungiyar dillalan man fetur masu zaman kansu a Najeriya wato IPAM, ya ce tuni suka yi hasashen faruwar hakan bayan rugujewar waccan yarjejeniyar.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar.

  • Barista Abba Hikima kan tsarin kiranye ga ƴan majalisu a dokokin Najeriya

    27/03/2025 Duración: 03min

    A farkon makon nan, Hukumar Zaɓen Najeriya INEC, ta ce ba a kammala cika ƙa'idojin da kundin tsarin mulki ya gindaya ba, a kan tsarin kiranyen da ake ƙoƙarin yi wa Sanata Natasha mai wakiltar yankin Kogi ta Tsakiya a zauren Majalisar Dattijai. INEC ta bayyana haka ne, bayan da ta fara nazari akan ƙorafe-ƙorafen da aka gabatar mata na nemn yi wa Sanata Natasha yankan ƙauna, wadda a kwanakin baya ta zargi shugaban Majalisar Dattawan Najeriyar Godswil Akpabio da cin zarafinta ta hanyar nemanta da lalata.Domin jin yadda tsarin na Kiranyen yake...Nura Ado Suleiman ya tattauna da Barista Abba Hikima, ƙwararren lauya a Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

  • Dr Auwal kan ɗauko hayar sojoji don horas da sojojin Najeriya wajen yaƙi da ta’addanci

    26/03/2025 Duración: 03min

    Gwamnatin Najeriya ta ɗauko hayar ƙwararrun sojoji daga wasu ƙasashen duniya, domin horas da sojojin ƙasar wajen yaƙi da ta’addanci, da kuma yin ƙundunbala wajen ceto mutanen da ‘yan ta’addan ke yin garkuwa da su. Ministan Tsaron Najeriya Badaru Abubakar ne ya sanar da matakin, a lokacin da yake ƙaddamar da aikin fara horas da kashin farko na sojojin Najeriyar a Kaduna.  A kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Auwal Aliyu Abdullahi, mai magana da yawun Kwamitin musamman na kula da walwalar tsaffin sojoji a Najeriya.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawarsu.............

  • Barista Al-Zubair kan matakin daina holin waɗanda ake zargi da ƴansanda ke yi

    25/03/2025 Duración: 03min

    Sufeta Janar na ƴansandan Najeriya Kayode Egbetokun, ya jaddada umarnin Antoni Janar na ƙasar, kan haramcin holin waɗanda ake zargi da aikata laifuka da jami’an tsaro ke yi ga manema labarai, ba tare da an hukuncin kotu ba. Ya ce a lokuta da dama jam’an tsaro basa iya gabatar da hujjoji kan zarge-zagen a gaban kotu, duk da cewa an nuna wa duniya fuskokinsu, lamarin da ya ce ya sabawa dokokin kare hakkin ɗan adam. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar tsakanin Khamis Saleh da Barista Al-Zubair Abubakar........ 

  • Air Commodore Tijjani Baba Gamawa mai ritaya kan cikar ECOWAS shekaru 50

    24/03/2025 Duración: 03min

    Yayin da ƙungiyar ECOWAS ke cika shekaru 50 a wannan mako, mun shirya muku rahotanni da hirarraki daban-daban dangane da gudunmawar da ƙungiyar ta bayar a cikin waɗannan shekaru. Daga cikin su akwai rawar da dakarun ECOMOG suka taka wajen magance rikice-rikice da aka samu a ƙasashen Liberia da Saliyo.Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Air Commodore Tijjani Baba Gamawa mai ritaya, ɗaya daga cikin sojojin da suka yi aikin samar da zaman lafiyar. ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.

  • Dakta Idris Harbau akan dakatar da sayar wa Ɗangote ɗanyen mai

    21/03/2025 Duración: 04min

    A ranar Larabar da ta gabata, matatar mai ta Ɗangote a Najeriya ta sanar da dakatar da sayar da mai da Naira ga 'yan kasuwa.Tuni dai lamarin ya haifar da fargaba a kan yiwuwar fukantar ƙarin farashin litar mai, bayan sauƙin da ‘yan Najeriya suka samu. Sai dai kamfanin ya ce matakin na wucin gadi ne, har sai an samu daidaito tsakaninsa da kamfanin NNPCL a kan adadin ɗanyen man da yake saye daga wurinsa da Naira.Kan wannan batu Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Aminu Idris Harbau, masanin tattalin arziƙi a Najeriya.Latsa alamar sauti don sauraren hirar: 

  • Dalung kan matakin dakatar da gwamnan Rivers da shugaba Tinubu ya ɗauka

    20/03/2025 Duración: 03min

    Ƙungiyar Lauyoyin Najeriya ta bayyana rashin amincewar ta da matakin da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya ɗauka, na dakatar da gwamnan Jihar Rivers Siminalayi Fubara da majalisar dokokin jihar, tare da naɗa kantoman soji. Kungiyar tare da jam’iyyun adawa da kuma wasu masu sharhi na cewa matakin ya saba dokar ƙasa. Dangane da wannan matsayi, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin shari’a Barr Solomon Dalung. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..........

  • Dakta AbdulHakim Funtua kan harin Isra'ila da ya hallaka Falasɗinawa sama 400

    19/03/2025 Duración: 03min

    Ƙasashe da hukumomi na ci gaba da yin tsokaci daban daban a kan halaka Falasɗinawa sama da 400 da Isra’ila ta yi jiya Talata a Gaza, lamarin da ya rusa yarjejeniyar tsagaita wutar da ta shafe watanni biyu tana aiki a yankin. Wani batu da ya ɗauki hankali bayan harin kuma shi ne, alwashin da Fira Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya sha na amfani da ƙarfi fiye da na baya wajen ƙwato ragowar mutane kusan 60 da ƙungiyar Hamas ke riƙe da su a Zirin na Gaza. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman da Dakta AbdulHakim Garba Funtua kan wannan lamari......

  • Tattaunawa da Dakta Kurfi kan hada-hadar kuɗaɗen Crypto a Najeriya

    18/03/2025 Duración: 03min

    Alƙaluma na nuni da cewa amfani da kuɗaɗen Crypto na daɗa samun karɓuwa a ƙasashen Yankin Kudu Da Saharar Afrika musamman ma Najeriya, inda a bara wani rahoto ya ce a tsakanin 2023 zuwa 2024, yawan kuɗaɗen Crypton da aka yi hada-hadarsu ya kai na Dalar Amurka biliyan 59. Wannan ya sa wasu ƙwararru bai wa mahukuntan Najeriyar shawarar, kamata yayi su rungumi sauyin domin amfana da shi a maimakon ƙoƙarin daƙile kasuwar Crypton, saboda illolin da suka ce na tattare da ita. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Nura Ado Suleiman  da Dakta Ƙasim Garba Kurfi, masanin tattalin arziƙi a Najeriya..............

  • Mahamadou Gamatche kan saukin ƙarancin mai a Jamhuriyar Nijar

    17/03/2025 Duración: 03min

    Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar sun ce an fara samun saukin karancin man fetur da aka fuskanta a kwanakin da suka gabata, abinda ya jefa jama'a da dama cikin halin kunchi. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Muhammadu Gamatche, shugaban gamayyar kungiyoyin masu motocin sufuri ta kasa a Nijar, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana

  • Malam Sirajo Issa kan rahoton taron ƙasar da aka yi a Nijar

    14/03/2025 Duración: 03min

    Kwanai bayan miƙa rahoton taron ƙasar da aka yi a Jamhuriyar Nijar, mutane na ci gaba da gabatar da ra'ayoyin su akai. Malam Sirajo Issa na ƙungiyar Mojen ya ce basa goyon bayan taron.

  • Farfesa Balarabe Sani Garko kan magance matsala mutuwar mata da jarirai

    12/03/2025 Duración: 02min

    Gwamnatin Najeriya ta bai wa jihohin kasar Dala biliyan guda domin amfani da shi wajen magance matsalar da ake samu na mutuwar mata da jarirai lokacin haihuwa.Ministan lafiyar kasar Mohammed Pate ya sanar da haka.Domin jin tasirin da zai yi,Bashir Ibrahim Idriss ya tattauna da Farfesa Balarabe Sani Garko na Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.

  • Tattaunawa da shugaban Amnesty a Najeriya kan kwato kuɗaɗen da EFCC ta yi

    11/03/2025 Duración: 03min

    Hukumar EFCC dake yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ta sanar da kwato kuɗaɗen da suka kai naira Triliyan guda a shekarar da ta gabata, abinda ke nuna irin nasarar da ta samu, baya ga samun nasara a kotu a shari’o’in da suka kai sama da 4,000.Dangane da wannan nasarar, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Isa Sanusi, Daraktan Ƙungiyar Amnesty a Najeriya, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiya hirar...........

página 1 de 2