Bakonmu A Yau

  • Autor: Vários
  • Narrador: Vários
  • Editor: Podcast
  • Duración: 1:30:36
  • Mas informaciones

Informações:

Sinopsis

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.

Episodios

  • Dr Yahuza Getso kan yadda jami'an sojoji suka hallaka Kachalla Ɗanbokolo a Zamfara

    02/07/2025 Duración: 03min

    A Najeriya mayaƙan sa kai a jihar Zamfara sun yi nasarar hallaka wasu daga cikin manyan kwamandojin ƴan bindigar da suka hana zaman lafiya a jihar, cikinsu har da Kachalla Ɗanbokolo da wasu tarin magoya bayansu. Domin sanin tasirin wannan nasara ga jama'ar yankin, Bashir Ibrahim Idris ya tattauba da masanin harkar tsrao, Dr Yahuza Getso.   Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar

  • Muhammad Adamu Dansitta kan shirin gwamnatin Najeriya na dasa bishiyoyi biliyan 20

    01/07/2025 Duración: 03min

    Gwamnatin Najeriya ta sha alwashin dasa itatuwa biliyan 20, a kokarin da take yi na magance gurgusowar hamada da tsananin zafi , har ma da sauyin yanayi. Mataimakin shugaban kasar Kashin Shetimma ne ya bayyana hakan, yayin da yake jawabi a wajen wani taroa  kasar Habasha. Game da tasirin wannan, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Muhammad Adamu Dansitta. Dannan alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.

  • Issof Emoud kan sabuwar Majalisar Tuntuɓa da gwamnatin sojin Nijar da kafa

    30/06/2025 Duración: 03min

    Majalisar Tuntuɓa da gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar ta kafa ta conseil consultatif na fara aiki a ranar Asabar 28 ga watan Yunin wannan shekara ta 2025, Majalisar mai kunshe da mambobi 194 an ɗaura mata nauyin bayar da shawarwari kan harokin da su ka shafi cigaban ƙasa da  kuma gayyato majalisa zartaswa domin amsa tambayoyi idan hakan ta kama. A kan haka Oumar Sani ya  tattauna da Hon. Issouf Emoud ɗan majalisa mai wakilta jihar Agadas.

  • Amb Abubakar Chika: cika shekaru 80 da sanya hannu kan yarjejeniyar samar da MDD

    26/06/2025 Duración: 03min

    Yau ake cika shekaru 80 da rattaɓa hannu kan yarjejeniyar da ta samar da Majalisar Ɗinkin Duniya da aka gudanar a Birnin San Francisco da ke Amurka, a ranar 26 ga watan Yunin shekarar 1945. Bikin cika shekaru 80 din na zuwa ne a daidai lokacin da Majalisar mai wakilai 193 ke fuskantar kalubale da dama, waɗanda suka hada da makomar ta ko kuma ci gaban tasirinta baki ɗaya. Kan wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Abubakar Chika, tsohon jakadan Najeriya a Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana..........

  • Aliyu Dawobe kan janyewar wasu ƙungiyoyin agaji a Arewa maso Gabashin Najeriya

    25/06/2025 Duración: 03min

    Ƙungiyar agaji ta ICRC wadda ke aiki a yankin arewa maso gabashin Najeriya, ta bayyana damuwa da janyewar wasu ƙungiyoyin agaji da ke bai wa ƴan gudun hijira tallafi a yankin. Babban jami'in yada labaran ƙungiyar a Najeriya, Aliyu Dawobe da ke ziyarar aiki a Lagos, ya mana ƙarin bayani dangane da halin da suke ciki.  Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Bashir Ibrahim Idris...........

  • Janar Sani Usman Kukasheka kan rundunar tsaro ta haɗin gwiwar ƙasashen ECOWAS

    24/06/2025 Duración: 03min

    Shugabannin ƙsashen Yammacin Afrika da ke ƙarƙarshin ƙungiyar ECOWAS sun sake bayyana damuwarsu dangane da ƙruwar matsalar tsaro a yankin. Yayin taron da suka gudanar a ƙarshen mako, shugaban ƙungiyar mai barin gado kuma shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake gabatar da buƙatarsa ta tabbatar da rundunar tsaro ta haɗin gwiwar da zata tinkari wannan matsalar. Bashir Ibrahim Idris ya tattaunawa da Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya,tsohon kakakin rundunar sojin Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..........

  • Muhammad Ibrahim Sa’id kan yunƙurin kwaso ƴan Najeriya da ke Iran

    23/06/2025 Duración: 03min

    Yanzu haka ƙasashe na ci gaba da ɗaukar matakan kwashe al’ummominsu daga Iran da kuma Isra’ila, saboda yadda yaƙi ya tsananta a tsakanin ƙasashen biyu. Bayanai na nuni da cewa ofishin jakadancin Najeriya da ke Iran, ya fara tsara yadda za su kwashe ƴan Najeriya da motoci zuwa Armenia kafin wataƙila a yi amafani da jiragen don dawo su gida. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muhammad Ibrahim Sa’id, ɗan Najeriya da ke karatu a birnin Qoom mai tazarar kilomita 150 a kudancin Tehran. Ku latsa alamar sauti domin jin zantawarsu........

  • IPMAN ta yaba wa Dangote na fara rarraba man fetur da Disal zuwa sassan ƙasar

    19/06/2025 Duración: 03min

    Ƙungiyar dillalan man fatir masu zaman kansu ta Najeriya IPMAN ta yaba da sabon shirin matan man Dangote na fara rarraba man fetur da Disal daga Lagos zuwa sassan ƙasar, sai dai ta ci gaba da nuna damuwa kan sabon harajin naira 12,500 da gwamnatin jihar Lagos ta sanya kan duk mota guda kafin bin titin Lekki da ke kaiwa matatar Dangote da sauran kamfanonin mai dake yankin, matakin da ya haifar da fargabar samun karin faranshin litar mai, masamman a arewacin ƙasar. Sai dai a tataunawarsa da Ahmad Abba, shugaban ƙungiyar IPMAN, Alhaji Abubakar Maigandi, ya ce bayan ɗan yajin aikin da derebobin dakon mai suka yi, gwamnatin Lagos ta sanya ranar Yau Alhamis, domin cimma matsaya kan wannan batu. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawarsu................

  • Jaloud Sambo kan juya baya ga takarar Paul Biya da ƴan adawar Kamaru suka yi

    18/06/2025 Duración: 03min

    A yayin da guguwar siyasa ke kaɗawa a Jamhuriyar Kamaru, alamu na nuni da cewa jiga-jigan jam’iyyu da suka daɗe suna ƙawance da jam’iyyar MPRC  mai mulkin ƙasar za su yi wata tafiya ta daban saɓanin ta shugaba Paul Biya ba. Bisa ga dukkannin alamu, ƙusoshin ƴan siyasa daga arewacin Kamaru da suka shafe shekaru a tafiyar kuma ke riƙe da manyan makamai irin su Isa Ciroma Bakari da Bello Buba Maigari sun fara tunanin yin watsi da tafiyar shugaba Biya, kamar yadda ake raɗe-raɗi. Akan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da Jaloud Sambo, shugaban ƴaƴan jam’iyyar adawa ta MPSC da ke zaune a ƙasashen waje.......

  • Tattaunawa da Dr Awwal Abdullahi kan kashe-kashen jihar Benue

    17/06/2025 Duración: 07min

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya umarci jami'an tsaro da su kawo karshen kashe-kashen da ake yi a jihar Benue ta tsakiya, inda rahotanni ke cewa fiye da mutane 200 ne suka mutu a wasu jerin hare-hare da aka kai Yelewata a baya-bayan nan. Kiran na zuwa bayan da daruruwan mutane suka gudanar da zanga-zanga a Makurdi babban birnin jihar domin nuna adawa da kashe-kashen.  A tattaunarsa da Ahmed Abba, Dr. Awwal Abdullahi Aliyu, masanin harkokin tsaro, kuma babban magatakardar ƙungiyar tsoffin sojojin Najeriya, ya fara da bayyana dalilan da ke haddasa rikicin. Shiga alamar sauti domin jin cikakken bayani.....

  • Alhaji Abubakar Cika kan rikicin Isra'ila da Iran

    16/06/2025 Duración: 03min

    A wannan litinin an shiga rana ta huɗu da fara yaƙi gadan-gadan tsakanin Isra’il ta Iran, inda kowanne daga cikin ƙsashen biyu ke amfani da manyan makamai don kai wa farmaki a kan manyan biranen ƙasashensu. Domin yin dubi a game da wannan rikici da ake ganin cewa muddun ba a dakatar da shi ba zai shafar ƙasashe da dama, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hira da Ambasada Alhaji Abubukar Cika.....

  • Farfesa Kamilu Sani Fagge kan bikin ranar dimokaraɗiyar Najeriya

    12/06/2025 Duración: 03min

    Yau Najeriya ke bikin Ranar Dimokaraɗiya, wadda gwamnatin ƙasar ta ware domin girmamawa a ranakun 12 ga watan Yunin kowace shekara, don tunawa da soke zaɓe na makamancin lokacin da gwamnatin mulkin soji ta yi a shekarar 1993. La’akari da cewa zuwa yanzu Najeriyar ta cika shekaru 26 kenan cif a ƙarƙashin mulkin Dimokaraɗiya, ya sanya Nura Ado Suleiman tattaunawa da Farfesa Kamilu Sani Fagge na Jami’ar Bayero da ke Kano. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar tattaunawasu..............

  • Sarkin Hausawan Mokwa kan makomar al'ummar da ambaliya ta shafa

    11/06/2025 Duración: 03min

    Bayanai daga Najeriya na cewa wasu daga cikin al’ummar da ibtila’in ambaliyar garin Mokwa ta jihar Neja ya shafa sun bijirewa yunƙurin mahukunta na kwashe su daga inda lamarin ya auku.Sai dai wani  jagoron al’umma a yankin ya musanta labarin, yana mai cewa jama’a a shirye suke duk lokacin da gwamnati ta shirya kwashe su. Ku latsawa alamar sauti domin jin karin bayani.....

  • Dr Mustapha Karkarna kan tanon duniya game da barazanar da Tekuna ke fuskanta

    10/06/2025 Duración: 03min

    Yayin da aka buɗe babban taro kan alkinta tekunan duniya a birnin Nice na Faransa, Majalisar Ɗinkin Duniya ta buƙaci a sake rattaba hannu kan sabbin yarjejeniyoyi da za su mayar da hankali kan alkinta tekuna da kuma kare hallittun ƙarƙashin ruwa. To sai dai duk da kasancewar Nahiyar Africa yankin da yafi fama da matsalolin muhalli ciki har da gurgusowar tekun, da alama taron bai yiwa yankin tanadin komai ba. Kan haka muka tattauna da Dr Mustapha Zakari Karkarna. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Rukayya Abba Kabara................

  • Malaman makarantu sun sake tsunduma yajin aiki a Nijar

    09/06/2025 Duración: 03min

    Gamayyar ƙungiyoyin malaman makarantu da ke koyarwa a matakai daban daban a Jamhuriyar Nijar, sun sanar da shiga yajin aikin kwanki 5 a jere daga wannan litinin, tare da barazanar da baiwa kowane ɗalibi maki ɗari bisa ɗari na jarabawar da aka yi masa. Malaman suna wannan yajin aiki  ne don neman gwamnati ta biya musu buƙatunsu da suka haɗa da: ɗaukar malaman kwantaragi a matsayin ma’aikata na dindindin, tare da biyan wasu kuɗaɗensu na alawus da suka maƙale a hannun gwamnati. A game da wannan batu, Ibrahim Malam Tchillo, ya zanta da shugaban ƙungiyar ASO EPT, mai fafutar samar da ilimi mai nagarta ga al’ummar Nijar wato Ibrahim Babaye Sani.Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana..................

  • Badaru Abubakar kan yadda ƴan Boko Haram suka ƙara ƙaimi wajen kai hare-hare

    08/06/2025 Duración: 03min

    Matsalar tsaro na ci gaba da addabar ƙasashen da ke yankin Sahel, lamarin da ke ƙara maida hannun agogo baya wajen yaƙi da ta'addanci da su ke yi. A wata zantawa da ministan tsaron Najeriya Mohammed Badaru Abubakar, ya ce ƴan ta’addan rinsu Boko Haram sun sauya salon kai hare-haren ta'addancinsu ne, sai dai ya ce a yanzu dakurun sojojin Najeriya sun gano salon kuma suna samun galaba akan ƴan ta'addan, lamarin da ya ce nan ba da jimawa za a kawo ƙarshen matalar. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsa da Aminu Sani Sado..........

  • Dr. Kabir Adamu kan kiran da Janar Christopher ya yi na gine iyakokin Najeriya

    05/06/2025 Duración: 06min

    Babban hafsan tsaron sojin Najeriya Janar Christopher Musa, ya yi kira da a gina katanga a ɗaukacin iyakokin ƙasar domin kawo karshen matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta. Janar Musa ya bayyana hakan ne yayin wani taro kan tsaro da aka gudanar a Abuja babban birnin ƙasar, inda ya bayyana katange iyakokin ƙasar a matsayin mai matuƙar muhimmanci, yana mai misali da yadda ƙasashen Pakistan da Saudiya suka katange iyakokinsu da Afghanistan da Iraq a matsayin abin koyi. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawar Ahmad Abba da Dr. Kabir Adamu, shugaban kamfanin tsaro na Beacon Security and Intelegence a Najeriya........

  • Najeriya na shirin shigar da shanu daga Denmark

    04/06/2025 Duración: 03min

    Gwamnatin tarayyar Najeriya ta sanar da shirinta na shigar da wasu shanu daga ƙasar Denmark, a ƙoƙarinta na rage kashe kuɗaɗen shigar da madara da kuma wadatarta a ƙasar, wanda yawansu ya kai dala biliyan 1.5 duk shekara. Duk da ikirarin kasancewarta ƙasar da ta fi kowacce yawan shanu a nahiyar Africa, amma Najeriya na samar da tan dubu 700 na madara duk shekara ne, ƙasa da tan miliyan 1.6 da ƴan ƙasar ke buƙata. To sai dai a zantawarsa da RFI Hausa, sakataren Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Najeriya Baba Usman Ngerzelma ya ce babu buƙatar ɗaukar wannan mataki da za’a mayar da hankali kan shanun da ake da su a ƙasar.Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu da Rukayya Abba Kabara..........

  • Ƙungiyar Amnesty ta zargi sojojin Najeriya da kashe ƴan-sa-kai a Zamfara

    03/06/2025 Duración: 04min

    Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International a Najeriya ta yi zargin cewa jirgin sojin saman ƙasar ya yi ruwan bamai-bamai kan jami’an sakai tare da kashe akalla 20 da jikkata wasu da dama a ƙauyukan Maraya da Wabi da ke ƙaramar hukumar Maru na jihar Zamfara. Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar jiya Litinin, ta ce lamarin kai tsaye ya shafi jami’an sakai da suka taru domin tunkarar ƴan bindiga da suka kai hare-hare a ƙauyukan nasu ranar Asabar.  A tattaunawarsa da Ahmad Abba, Daraktan Amnesty International a Najeriya, Malam Isa Sunusi, ya fara da bayani kan yadda lamarin ya auku.

  • Har yanzu akwai sauran gawarwakin da ba a gano ba - Dauda Mokwa

    02/06/2025 Duración: 03min

    Kwanaki biyar bayan da ambaliyar ruwa ta afka wa garin Mokwa na jihar Neja a tarayyar Najeriya, mahukunta a yankin sun ce adadin mutanen da aka tabbatar da cewa sun rasa rayukansu sun kai ɗari biyu. A cewa Sakataren ƙaramar hukumar ta Mokwa Dauda Liman Mokwa, yanzu ana kyautata zaton cewa akwai gawarwaki da dama da ba a kai ga gano su ba, ko dai a cikin ruwa ko kuma a ƙarƙashin gine-ginen da suka rufta. Ku latsa alamar sauti don jin tattaunawarsa da Abdulkarim Ibrahim Shikal..............

página 1 de 2