Sinopsis
A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.
Episodios
-
Jaloud Sambo kan juya baya ga takarar Paul Biya da ƴan adawar Kamaru suka yi
18/06/2025 Duración: 03minA yayin da guguwar siyasa ke kaɗawa a Jamhuriyar Kamaru, alamu na nuni da cewa jiga-jigan jam’iyyu da suka daɗe suna ƙawance da jam’iyyar MPRC mai mulkin ƙasar za su yi wata tafiya ta daban saɓanin ta shugaba Paul Biya ba. Bisa ga dukkannin alamu, ƙusoshin ƴan siyasa daga arewacin Kamaru da suka shafe shekaru a tafiyar kuma ke riƙe da manyan makamai irin su Isa Ciroma Bakari da Bello Buba Maigari sun fara tunanin yin watsi da tafiyar shugaba Biya, kamar yadda ake raɗe-raɗi. Akan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da Jaloud Sambo, shugaban ƴaƴan jam’iyyar adawa ta MPSC da ke zaune a ƙasashen waje.......
-
Tattaunawa da Dr Awwal Abdullahi kan kashe-kashen jihar Benue
17/06/2025 Duración: 07minShugaban Najeriya Bola Tinubu ya umarci jami'an tsaro da su kawo karshen kashe-kashen da ake yi a jihar Benue ta tsakiya, inda rahotanni ke cewa fiye da mutane 200 ne suka mutu a wasu jerin hare-hare da aka kai Yelewata a baya-bayan nan. Kiran na zuwa bayan da daruruwan mutane suka gudanar da zanga-zanga a Makurdi babban birnin jihar domin nuna adawa da kashe-kashen. A tattaunarsa da Ahmed Abba, Dr. Awwal Abdullahi Aliyu, masanin harkokin tsaro, kuma babban magatakardar ƙungiyar tsoffin sojojin Najeriya, ya fara da bayyana dalilan da ke haddasa rikicin. Shiga alamar sauti domin jin cikakken bayani.....
-
Alhaji Abubakar Cika kan rikicin Isra'ila da Iran
16/06/2025 Duración: 03minA wannan litinin an shiga rana ta huɗu da fara yaƙi gadan-gadan tsakanin Isra’il ta Iran, inda kowanne daga cikin ƙsashen biyu ke amfani da manyan makamai don kai wa farmaki a kan manyan biranen ƙasashensu. Domin yin dubi a game da wannan rikici da ake ganin cewa muddun ba a dakatar da shi ba zai shafar ƙasashe da dama, Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da tsohon jakadan Najeriya a Iran. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar hira da Ambasada Alhaji Abubukar Cika.....
-
Farfesa Kamilu Sani Fagge kan bikin ranar dimokaraɗiyar Najeriya
12/06/2025 Duración: 03minYau Najeriya ke bikin Ranar Dimokaraɗiya, wadda gwamnatin ƙasar ta ware domin girmamawa a ranakun 12 ga watan Yunin kowace shekara, don tunawa da soke zaɓe na makamancin lokacin da gwamnatin mulkin soji ta yi a shekarar 1993. La’akari da cewa zuwa yanzu Najeriyar ta cika shekaru 26 kenan cif a ƙarƙashin mulkin Dimokaraɗiya, ya sanya Nura Ado Suleiman tattaunawa da Farfesa Kamilu Sani Fagge na Jami’ar Bayero da ke Kano. Ku latsa alamar sauti don jin cikakkiyar tattaunawasu..............