Tattaunawa Da Ra'ayin Masu Saurare

  • Autor: Vários
  • Narrador: Vários
  • Editor: Podcast
  • Duración: 4:02:29
  • Mas informaciones

Informações:

Sinopsis

Shiri ne na musamman, da kan tattaunawa da bangarori daban-daban na Alumma da ke sauraren Shirye shiryen RFI Hausa daga kowane kusurwa na fadin duniya, kan muhimman batutuwa, da suka shafi siyasa Tattalinariziki, aladu da dai sauransu

Episodios

  • Ra'ayoyin masu saurare kan shirin rungumar GMO a Najeriya

    19/08/2025 Duración: 10min

    Lura da yadda jama’a ke ɗari-ɗari a game da kayan abincin da aka sauya wa ƙwayoyin halitta da ake kira GMO, wannan ya sa mahukunta a Najeriya ke neman yin amfani da malaman addini domin gamsar da jama’a su rungumi irin wannan abinci. Abin neman sani a nan shi ne, shin ko kun fahinci abin da ake kira GMO? Ko a shirye ku ke domin karɓar nau’in abincin da aka canza wa ƙwayoyin halitta? Anya yin amfani da malaman addini zai sa jama’a su amince da shi a Najeriya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

  • Ra'ayoyin masu saurare kan kama jagororin ƙungiyar Ansaru a Najeriya

    18/08/2025 Duración: 10min

    Mai Bai wa Shugaban Najeriya Shawara kan Sha’anin Tsaro Nura Ribaɗo ya tabbatar da kama jagororin ƙungiyar Ansaru da ake kira Ƴan Mahmuda su biyu, waɗanda suka jima suna addabar yankunan ƙasar. Ana dai bayyana wannan ƙungiya a matsayin babbar barazana ga matsalar tsaron ƙasar, saboda alaƙarta kai-tsaye da Alqa’ida. Shin ko wane sauyi wannan kame zai samar ta fannin tsaro a Najeriya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

  • Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    15/08/2025 Duración: 09min

    Yau take ranar bayyana ra'ayoyinku kan batutuwa da suke ci muku tuwo a ƙwarya, kama daga siyasa, tattalin arziƙi, zamantewa da sauran abubuwan daban daban na rayuwa. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyin...

  • Ra'ayoyin masu saurare kan yajin aikin lauyoyi a Nijar

    14/08/2025 Duración: 09min

    Lauyoyi a Jamhuriyar Nijar sun tsunduma yajin aikin kwanaki biyu daga yau Alhamis, domin nuna rashin amincewa da rusa ƙungiyoyin alƙalai da sauran ma’aikatan shari’a da gwamnatin ƙasar ta yi. Kafin rusa waɗannan ƙungiyoyi, tuni aka rusa ƙungiyoyin jami’an kare gandun daji da na kwastam da kuma illahirin jam’iyyun siyasar ƙasar. Shin, ko me za ku ce a game da wannan mataki na gwamnatin Nijar ta ɗauka? A irin wannan yanayi, ko meye makomar ƴancin gudanar da ƙungiyoyi a ƙasar? Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi...

  • Ra'ayoyin masu sauraro kan yadda Bankin Duniya ya rantawa Najeriya dala miliyan 300

    13/08/2025 Duración: 10min

    Bankin Duniya ya amince ya ranta wa Najeriya dala miliyan 300 kwatankwacin naira biliyan 460 don tallafa wa mutanen da suka ƙaurace wa matsugunansu saboda matsaloli a sassa daban daban na Arewacin ƙasar. Yanzu haka akwai mutane sama da milyan 3 da rabi da ke rayuwa a wannan yanayi, kuma mafi yawansu sun dogara da tallafi ne domin rayuwa. Shin ko waɗanne matakai suka kamata a ɗauka don tabbatar da cewa an yi amfani da kuɗaɗen ta hanyoyin da suka dace? Sai ku bayyana ra’ayoyinku a lambarmu ta Whatsapp da kuma shafinmu na Facebook.

  • Ra'ayoyin masu saurare kan yadda ake samun ambaliyar ruwa a irin wannan lokaci

    12/08/2025 Duración: 10min

    Kusan a kowacce shekara, dai-dai wannan lokaci ne ake samun faruwar ambaliya sakamakon saukar ruwan sama mai yawa da ke haddasa asarar rayuka da kuma dukiyoyi masu tarin yawa. A daidai wannan lokaci, ko wane hali ake ciki a yankunanku dangane da batun ambaliya? Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a wannan rana. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

  • Ra'ayoyin masu saurare kan matakin Nijar na ƙwace kamfanonin haƙar zinare

    11/08/2025 Duración: 10min

    Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta sanar da ƙwace ilahirin kamfanonin haƙo zinare tare da shelanta cewa sun zama mallakin ƙasar, yayin da a ɗaya ɓangare ta hana fitar da duk wani nau’in dutse mai ƙima zuwa ƙetare sai tare da izinin hukuma. Hakan na zuwa ne watanni bayan ta ƙwace kamfanonin haƙo uranium matsayin mallakin ƙasar. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

  • Waɗanne abubuwa ne suka fi ci muku tuwa a ƙwarya

    08/08/2025 Duración: 10min

    Shirin ra'ayoyin ku masu saurare na wannan rana kamar yadda aka saba ya baku damar fadɗn albakacin bakinku kan abubuwan da suka fi ci muku tuwo a ƙwarya a fannin lafiya, jagoranci, siyasa da kuma zamantakewa. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nasiru Sani

  • Ra'ayoyin masu saurare kan kalaman Falana game da matakan tattalin arziƙin Tinubu

    07/08/2025 Duración: 10min

    Bisa ga al’ada, ana cewa al’umma ta kasu ne zuwa rukuni uku, wato attajirai, da matsakaita sai kuma matalauta. To sai dai a cewar shahrarren lauya kuma mai fafutuka Femi Falana, a Najeriya mutane na rayuwa ne a ɗaya daga cikin rukuni biyu kawai: wato gungun attajirai ko kuma na talakawa, wannan kuwa sakamakon ɓullo da sabuwar siyasar tattalin arziki maras alfanu a ƙasar.

  • Ra'ayoyin masu saurare kan zanga-zangar neman korar 'yan Najeriya daga Ghana

    31/07/2025 Duración: 09min

    A ƴan kwanakin nan an samu ɓarkewar zanga-zangar a Ghana, inda ƴan ƙasar ke zargin ƴan Najeriya da ke can da aikata laifuka kisan gilla da karuwanci, lamarin da ya sa masu zanga-zangar neman a koresu daga ƙasarsu. Haka nan masu zanga-zangar sun yi ikirarin cewa ƴan kasuwan Najeriya  sun mamaye musu kasuwanni tare da karya dokokin kasuwanci a ƙasar. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

  • Ra'ayoyin masu saurare kan karrama 'yan wasan Super Falcons da Tinubu yayi

    29/07/2025 Duración: 10min

    Tarihi dai ya maimaita kansa, inda tawagar Super Falcons ta Najeriya ta lashe gasar WAFCON karo na 10, bajintar da ba tawagar da ta taɓa yi. Sakamakon haka ne shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karrama ƴan wasan da lambar girmamawa ta ƙasa OON, da dala dubu dari-dari ($100,000) kowacce, da kuma gidaje a Abuja. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

  • Ra'ayoyin masu saurare kan bikin cika shekaru biyu da juyin mulkin Nijar

    28/07/2025 Duración: 10min

    A ranar Asabar da ta gabata, 26 ga watan Yuli Jamhuriyar Nijar ta yi bikin cika shekaru biyu a kasancewa a ƙarƙashin mulkin soji, wadanda suka hambarar da gwamnatin Mohamed Bazoum kuma suke cigaba da tsare  shi ba tare da gurfanar da shi ba. A waje daya kuma a karon farko a jawabin da ya  gabatar jagoran gwamnatin sojin Janar Abdourahmane Tchiani ya ce ya san halin ƙunci da jama’a ke ciki. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

  • Yau take ranar jin ra'ayoyin ku masu saurare kan batutuwa mabanbanta

    25/07/2025 Duración: 09min

    A duk ranar Juma'a, RFI Hausa na bai wa jama'a damar tofa albarkacin bakinsu kan abubuwan da ke ci musu tuwo a ƙwarya kama daga siyasa, tattalin arziki, zamantakewa, harkokin yau da kullum da dai saurarensu. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...

  • Ra'ayoyin masu saurare kan rahoton NBS na ƙaruwar tattalin arziƙin Najeriya

    23/07/2025 Duración: 09min

    Hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta ce tattalin arzikin ƙasar ya samu ƙarin tagomashi da kashi 3 da ɗigo 13 a rubu’in farko na wannan shekarar ta 2025, saɓanin kashi 2 da ɗigo 27 yake a daidai wannan lokaci a shekarar 2024.   Wannan na zuwa ne yayin da talauci ke ci gaba da ta’azzara a tsakanin al’ummar ƙasar, kuma manoma sun gaza yin noma yadda ya kamata saboda matsalar ta’addanci. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

  • Ra'ayoyin masu saurare kan zanga-zangar 'yansanda a Najeriya

    22/07/2025 Duración: 09min

    A babban birnin Tarayyar Najeriya, Abuja, ɗaruruwan ƴansanda da suka yi ritaya kuma bisa ga dukkan alamu da yawun waɗanda suke bakin aiki a yanzu ne suka gudanar da zanga-zangar neman a cire su daga tsarin fanshon adashen gata, wanda suka ce babu abin da ya yi face jefa su cikin baƙin talauci bayan shafe shekaru suna wa ƙasar hidima. Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi....

  • Yadda Isra'ila ke kashe Falasɗinawa masu jiran tallafin abinci

    21/07/2025 Duración: 09min

    Shirin ra'ayoyin ku masu sauraro na wannan rana ya mayar da hankali ne kan yadda Isra'ila ta mayar da guraren rabon abincin tallafi a Gaza tarkon mutuwa. Ku danna alamar sauraro domin jin cikakken shirin tare da Hauwa Aliyu.

  • Ra'ayoyin masu saurare kan rashin yiwa yara rigakafin cutuka a Najeriya a 2024

    16/07/2025 Duración: 09min

    Wani sabon rahoton Asusun kula da ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce ƙananan yara  sama da miliyan 14 ne a fadin duniya ba su samu alluran rigakafin cutukkan da ke addabar yara a shekarar 2024 ba, kuma sama da miliyan biyu daga cikin wannan adadi a Najeriya suke. Rashin wannan rigakafi  na iya jefa waɗannan yara cikin hatsarin kamuwa da cutukan da ake iya samun kariya daga gare su. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...

  • Shugaban Kamaru Paul Biya zai sake tsayawa takarar shugabancin ƙasar karo na 8

    15/07/2025 Duración: 09min

    Shugaban Kamaru Paul Biya ya bayyana aniyar sa ta sake tsayawa takarar shugabancin ƙasar a karo na 8 yana mai shekaru 92 da haihuwa, inda ya yi iƙirarin cewa matasa da mata ne zai fi bai wa fifiko idan ya samu ya zarce. Wani saƙo da Biya mai shekaru 92 ya wallafa a shafinsa na Twitter ne ke sanar da wannan mataki wanda ya kawar da jita-jitar da ke nuna cewa shugaban a wannan karon bashi da sha'awar tsayawa takara don neman wa'adi na gaba. Fiye da shekaru 40 kenan Paul Biya ke jagorancin Kamaru kasancewarsa shugaba na biyu da ya jagoranci ƙasar tun bayan samun ƴancinta daga Faransa wato bayan murabus ɗin shugaba Amadou Ahidjo. Idan har Paul Biya ya yi nasarar lashe zaɓen da zai bashi damar sake yin shekaru 7 a karagar mulki, kenan shugaban mafi daɗewa kan mulki, zai tasamma shekaru 100 na rayuwarsa a karagar mulki karon farko da ake ganin irin hakan a tarihi. Shiga alamar sauti, domin sauraro cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.

  • Ra'ayoyin masu saurare kan mutanen da 'yanbindiga suka kashe a cikin watanni 6

    09/07/2025 Duración: 10min

    A Najeriya, wasu alƙaluman hukumar kare hakkin ɗan adam ta ƙasar sun ce adadin mutanen da ƴanbindiga suka kashe a cikin watanni shida na farkon wannan shekarar ya zarce na ilahirin shekarar da ta gabata, inda a watan da ya gabata kawai mutane  606 ne masu ɗauke da makamai suka halaka. Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...

  • Ra'ayoyin masu saurare kan yadda ambaliya ke yin ɓarna a wasu biranen Afrika

    07/07/2025 Duración: 10min

    Ambaliyar ruwa na ci gaba da yin ɓarna a wasu biranen ƙasashen Afrika, inda ko a baya-bayan nan ta laƙume rayuka fiye da 600 a ƙaramar hukumar Mokwa ta jihar Nejan Najeriya yayin da tituna suka fara cika da ruwa a wasu ƙananan hukumomin jihar Kano, baya ga babban birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar da aka samu iftila’in ambaliyar a kwanakin baya.   Ya ya matsalar ta ke a yankunan ku, ko wani mataki kuke ɗauka don ganin kun kare kanku daga iftila’in ambaliyar ruwan yayin da daminar bana ta sauka? Shin ko akwai wasu matakai da gwamnatocinku ke ɗauka?

página 1 de 2