Sinopsis
Shiri ne na musamman, da kan tattaunawa da bangarori daban-daban na Alumma da ke sauraren Shirye shiryen RFI Hausa daga kowane kusurwa na fadin duniya, kan muhimman batutuwa, da suka shafi siyasa Tattalinariziki, aladu da dai sauransu
Episodios
-
Shirin ra'ayoyin ku masu sauraro a yau.
03/02/2025 Duración: 09mina yau shirin namu na ra'ayoyin ku masu sauraro ya yi dubu ne akan Shin ko menene ra'ayin ku a game da batun tattaunawa da 'yan bindiga.
-
Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta
31/01/2025 Duración: 09minA yau juma'a kamar yadda aka saba kuna aiko mana da saƙonnin ra'ayoyinku kan abubuwan da ke ci muku tuwo a ƙwarya a fannoni daban-daban na rayuwa, kama daga fannin tattalin arziki, tsaro, lafiya, siyasa da sauransu. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan shirin samar da lantarki ga gidaje 300M a Afirka
30/01/2025 Duración: 09minShugaban Najeriya Bola Tinubu ya sake jaddada aniyarsa ta inganta samar da wutar lantarki a faɗin ƙasar. Tinubu ya bayyana haka ne wajen taron ƙasashen Afirka wanda ya mayar da hankali akan yadda za a samar wa aƙalla mutane miliyan 300 wutar lantarki a nahiyar baki ɗaya. Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan cikar wa'adin ficewar ƙasashen AES daga ECOWAS
29/01/2025 Duración: 09minYau 29 ga watan Janairu wa’adin farko da kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso suka bayar na ficewa daga kungiyar ECOWAS ya cika, abinda ke tabbatar da raba garin bangarorin biyu dangane da cikar wannan wa’adi, Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta
24/01/2025 Duración: 10minA yau juma'a kamar yadda aka saba kuna aiko mana da saƙonnin ra'ayoyinku kan abubuwan da ke ci muku tuwo a ƙwarya a fannoni daban-daban na rayuwa, kama daga fannin tattalin arziki, tsaro, lafiya, siyasa da sauransu. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...
-
Yadda aka fara samun saukin farashin kayayyakin abinci a Najeriya
23/01/2025 Duración: 10minRahotanni daga wasu sassan Najeriya ciki har da babbar kasuwar kayan abinci dangin hatsi ta Dawanau da ke Kano na cewa an fara samun sauƙin farashin kayayyakin abincin, idan aka kwatanta da yadda al’amarin yake a watannin baya. Lamarin dai ya haifar da muhawara akan dalillan da suka janyo saukin farashin kayana abincin da ɗorewar hakan.Abin tambayar shine, ko al'umma sun gamsu da wannan rahoto, ko kuma har yanzu anan nan a gidan jiya?Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin.
-
Ra'ayoyin masu saurare kan ficewar Amurka daga WHO
22/01/2025 Duración: 09minA ƙasar Amurka, bayan rantsar da shi a matsayin sabon shugaba ƙasa na 47, Donald Trump, ya rattaba hannu kan wasu gomman dokokin zartawa na ikon shugaban ƙasa, ciki har da janye ƙasarsa daga Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), kamar yadda ya yi a wa’adin mulkinsa na farko, kafin magabacinsa Joe Biden ya maido da ƙasar ciki. Wasu na ganin wannan mataki zai yi illa ƙwarai ga ɗorewar hukumar wajen gudanar da ayyukan ta a duniya, duba da kaso mai tsoka da Amurka ke bayarwa wajen gudanar da ayyukan WHO ɗin.Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan sabuwar dokar Nijar na hukunta baƙi marasa takardu
15/01/2025 Duración: 09minA wannan makon ne gwamnatin sojin Nijar ta gabatar da wata sabuwar doka da ke tilastawa baƙi da ke neman zuwa ƙasar da su tabbatar sun samu takardun izini da suka dace, tare da gargadi ga su ma ƴan ƙasar da su yi hattara wajen ƙarbar baƙunci baƙi da ke shiga ƙasar ba bisa ƙa’ida ba. Sabuwar dokar ta soji ta tanadi hukunci mai tsauri ga waɗanda suka saɓa umarnin a bangarorin baƙi da su kansu ƴan ƙasar, wanda ya ƙunshi hukuncin ɗauri a gidan yari da kuma tara.Gwamnati da wasu ƴan ƙasar na cewa anyi hakan ne saboda dalilai na tsaro, yayin da wasu ke danganta hakan da tsoro da fargaba, to ku ya kuka kalli wannan mataki?Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin.....
-
Ra'ayoyin masu saurare kan hare-haren soji da ke kashe fararen hula bisa kuskure
14/01/2025 Duración: 10minA baya-bayan hare-haren sojojin Najeriya kan ƴan ta’adda na shafar fararen hula musamman ƴan sa kai da ke taimakawa wajen yaƙar matsalolin tsaro. Matsalar na ƙara yawaita inda a kwanan nan sojojin suka kai hari a jihohin Sokoto da Zamfara wanda ya halaka fararen hula fiye da 100, yayin da a kowane lokaci sojojin kan musanta hakan , daga baya kuma su ce za su gudanar da bincike.Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan sallamar tuɓaɓɓun ƴan Boko Haram da aka yi a Nijar
13/01/2025 Duración: 09minA wani yanayi da ba safai aka saba gani ba, mahukuntan Nijar sun sallami tuɓaɓɓun mayaƙan Boko Haram aƙalla 124 ciki har da ƙananan yara 44, waɗanda aka basu horan sauya ɗabi’u don komawa rayuwar fararen hula. Wannan shi ne karon farko da ake ganin irin hakan, tun bayan makamancin yunƙurin da hamɓararren shugaban ƙasar Bazoum Muhammad ya yi watanni ƙalilan gabanin hamɓarar da shi.Latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyi a cikin shirin...
-
Yadda ake rige-rigen neman aiki a hukumar kwastam da ke Najeriya
09/01/2025 Duración: 10minKamar yadda labari ya karaɗe kafafen yada labarai, ƙaasa da mako guda bayan da hukumar kwastan a Najeriya ta sanar da buɗe shafin yanar gizo don aikewa da takardun neman ɗaukar jami’ai kimanin dubu 4, sama da masu neman wannan aiki dubu dari 5 ne suka gabatar da buƙatunsu. Wannan al’amari ne da ke faruwa a kowace ma’aikata a duk lokacin da aka sanar da buƙatar ɗaukar ma’aikata.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.
-
Kan yadda aka gudanar da bikin rantsuwar sabon shugaban Ghana
08/01/2025 Duración: 09minA wannan talatar ce aka rantsar da John Mahama a matsayin shugaban Ghana, cikin yanayi na tarin kalubale da suka hada da na matsin tattalin arziki biyo bayan lashe zaben da aka yi cikin kwanciyan hankali da lumana. Masu bibiyar siyasa a kasar sunyi ittifakin cewa duk da cewa Mahaman ya taba jagorancin kasar, ya dawo ne a lokacin da lamura suka sauya ainun.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Abida Shu'aibu Baraza.
-
Kan yadda duniya ta yi bankwana da shekarar 2024
31/12/2024 Duración: 10minA yayin da ake bankwana da shekarar 2024 shuwagabanni daga kasashen Duniya na fuskantar tarin kalubale da suka hada da rikice-rikice,yake-yake harma da wasu matsalolin da suka shafi sauyin yanayi da matsin tattalin Arziki da sauran su. Wasu abubuwa ne baza ku iya mantawa ba kuke tsoron dakon su zuwa sabuwar shekara?Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin, tare da Hauwa Garba Aliyu Zaria.
-
Ra'ayoyin masu saurare kan batutuwa mabanbanta
27/12/2024 Duración: 09minA yau juma'a kamar yadda aka saba kuna aiko mana da saƙonnin ra'ayoyinku kan abubuwan da ke ci muku tuwo a ƙwarya a fannoni daban-daban na rayuwa, kama daga fannin tattalin arziki, tsaro, lafiya, siyasa da sauransu. Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyi mabanbanta...
-
Ra'ayoyin masu saurare: harin soji kan Lakurawa ya hallaka mutane fiye da 10
26/12/2024 Duración: 09minAna fargabar al'umma da dama sun mutu wasu kuma sun jikkata sakamakon wani hari da jirgin yaƙi na soji ya kai kan Lakurawa a wasu ƙauyuka da ke Sokoton Najeriya. Ana kallon wannan harin a matsayin na kuskure kuma ba wannan ne karon farko da hakan ke faruwa ba a arewaci da wasu Najeriya.Latsa alamar sauti domin sauraren mababanta ra'ayoyi a cikin shirin da Abida Shu'aibu Baraza ta jagoranta...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan rasa rayuka da aka yi yayin turmutsitsi a Najeriya
23/12/2024 Duración: 10minAƙalla mutane 60 suka rasa rayukansu a sassan Najeriya, yayin turmutsitsin karɓar tallafin abinci da kuma taron bikin ƙarshen shekara na yara a jihohin Anambra, da Oyo da kuma birnin Abuja. A yayin da ‘yan Najeriyar ke tofa albarkacinsu kan lamarin wasu na ɗora laifin aukuwar haɗurran akan gazawar mahukunta wajen samar da tsarin bai wa mutane kariya yayin taruka, yayin da wasu ke ganin ɗaiɗaikun masu raba tallafin ke da alhaki la’akari da cewar suna yin hakan ne ba tare da tsari ko sanin hukuma ba.Wannna shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan kasafin kuɗin 2025 da shugaban Najeriya ya gabatar
19/12/2024 Duración: 11minA ranar Laraba ne shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gabatar da kasafin kudin ƙasar na shekarar 2025 na naira Tiriliyan 47.9. Sai dai wani batu da ya haifar da muhawara a tsakanin ‘yan Najeriya dangane da kasafin kuɗin na baɗi, shi ne yadda aƙalla kaso 30 zuwa 32 na yawan kuɗaɗen za su tafi a biyan basuka ko kuma kudin ruwan basukan, kwatankwacin naira tiriliyan 15 da biliyan 800, adadin da ya zarce yawan kudaden da aka warewa tsaro, ilimi, lafiya da manyan ayyuka.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Kabiru Mohammed Dan Bauchi...
-
Ra'ayoyin masu sauraren Rfi biyo bayan lashe kyautar gwarzon ɗan wasan Afrika na 2024 daga Lookman
17/12/2024 Duración: 10minA bikin da aka gudanar a birnin Marrakech na Morocco, Lookman ya shiga gaban ƴan wasan irinsu Simon Adingra na Ivory Coast da Achraf Hakimi na Morocco da Serhou Guirassy na Guinea sai kuma mai tsaron gidan Afrika ta Kudu Ronwen Williams.Tauraruwar Lookman wanda ke wasa a ƙungiyar Atalanta na haskawa a bana, musamman idan aka yi la’akari da bajintar da ya nuna wajen zamowa ɗan wasa na farko tun daga shekarar 1975 da ya zura kwallaye uku a raga cikin mintina 26.Masu saurare sun bayyana fatan da suke da shi a cikin wannan shiri..........
-
Ra'ayoyin masu saurare kan shirin maja tsakanin Atiku da Obi a zaɓen 2027
12/12/2024 Duración: 10minTsohon mataimakain shugaban Najeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a zaben 2023 da ya gabata Atiku Abubakar da kuma ɗan takarar LP a 2023 Peter Obi na shirin haɗewa domin kawar da gwamnatin APC wadda a cewarsu ta gaza, lamarin da ke zuwa tun kafin kakar zaɓen na shekarar 2027. Sai dai a martaninta, jam’iyyar APC ta ce babu wata haɗaka da za ta iya taka wa shugaba mai ci birki.Wannan shi ne maudu'in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a kai.Latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin...
-
Ra'ayoyin masu saurare kan haramcin fitar da masara daga Najeriya
11/12/2024 Duración: 10minKamar yadda aka saba, RFI Hausa na bai wa masu saurare damar bayyana ra'ayoyinsu kan batutuwa da dama da ke ci musu tuwo a ƙwarya. Majalisar dattawar Najeriya ta amince da wani kuɗirin doka da ya haramta fitar da duk wata masara mai yawa da ba'a sarrafa ta ba daga ƙasar zuwa ƙasashen waje, kuma ta tanadi hukuncin ɗaurin shekara guda ga duk wanda ya yi kunnen ƙashi.Wannan shi ne maudu’in da muka baku damar tofa albarkacin bakinku a yau.Latsa alamar sauti domin sauraren ra'ayoyin mabanbanta..